Saturday 9 April 2022

Sakon tuni ga yan najeriya daga sanata shehu sanii

 Ikon Allah,Babu irin zagin da ban sha ba,Babu irin cin mutuncin da ban gani ba a lokacin da muka fara magana kan rashin tsaro a Arewacin Najeriya.Wai yanzu su da kansu suke fadi bayan abubuwa sun tabarbare gaba daya.

Wanda suka zage mu Mun barsu da Allah.


2023: Ni zan fara yin Mataimakiyar Shugaban Ƙasa -- Yahaya Bello Gwamna Kogi State

 2023: Ni zan fara yin Mataimakiyar Shugaban Ƙasa -- Yahaya Bello



Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya ce zai ɗauki mace ta yi masa mataimakiya idan jam'iyar APC ta tsaida shi takarar shugaban ƙasa a 2023.


Bello ya baiyana hakan ne a wani taron karawa juna sani da ƴan jarida masu rahoton labaran siyasa da na kotu a jiya Juma'a a Abuja.


A cewar Bello, zai baiwa mata muhimmanci idan har a ka bashi dama ya zaɓi wanda zai yi takara da shi.


Gwamnan ya ce ya na da burin yin gwamnati da za ta tafi da kowa, musamman mata, matasa da masu buƙata ta musamman.


Ya ƙara da cewa haka ya ke gudanar da mulkinsa a Kogi in da bai bar kowa ba wajen tafiyar da gwamnatinsa.


Bello ya ƙara da cewa idan ya samu dama, zai samar da tallafi ga matasa da mata domin bunƙasa tattalin arziki.

Tuesday 5 April 2022

MUBARAK BALA YA AMSA LAIFINSA A KOTU

 Mubarak Bala ya amsa laifin aikata sabo a gaban kotu


Wata babbar kotu a Kano ta sake aikewa da Mubakar Bala zuwa gidan gyaran hali, saboda ci gaba da tsare rayuwarsa da kuma gazawar lauyoyinsa na gabatar wa kotun da cikakaken takardun da za su tabbatar mata cewar yana fama da rashin lafiya.


An karanto ma M


ubarak Bala caji 14 da ake tuhumarsa a kai na yin sabo.


Yayin zaman kotun, an karanto masa sakonnin da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na Facebook, wadanda yayi kalaman batanci ga addinin Musulunci.


Ya amsa dukkan caji 14 da aka karanto masa da cewar ya aikata dukkan laifukan da ake tuhumarsa da aikatawa.


Ganin haka sai lauyansa ya roki kotun ta ba shi damar ganawa da wanda yake wakiltar, wato Mubarak Bala, kuma bayan ta amince, ya yi kokarin nuna ma sa tasirin cewa ya amsa dukkan laifukan da ake tuhumarsa.


Amma bayan da lauyan ya sanar da kotun cewa Mubarak Bala na son sauya amsar da ya bayar a gaban kotun, sai alkalin ya sake tambayar wanda ake tuhumar ko haka lamarin yake.


Mubarak Bala ya sanar da kotun cewa ba zai sauya amsa laifinsa da ya yi a gaban kotun ba.


Alkali kotun ya tambaye shi ko ya fahimci nauyin abubuwan da yake cewa, kuma wanda ake tuhumar ya amsa cewa ya fahimci komai.


Ya kara da cewa babu wanda ya tursasa masa don ya amsa dukkan laifukan da ake tuhumarsa da aikatawa. Sannan ya ce babu wanda yayi masa wani alkawari, ko ya sanya masa wani ra’ayi, sai dai ya bukaci kotun ta yi masa sassauci da kuma adalci.


Wakilin BBC da ke kotun ya ce kotun na ci gaba da sauraron shari'ar.


Tushe: BBC Hausa

Monday 4 April 2022

Cire sheikh nuru Khalid daga limanci ba abinda zai rageshi dashi sedai samun daukaka danasara arayuwa

 Sheikh Nura Khalid


cire shi daga limanci babu abinda zai kara masa sai nasara 


Yanzu na fahinci hikima wasu malamai da suke nemo taimako daga kasa shen waje ko daga wasu mutane abokai ko dalibai su gina musu makaranta da masallaci hakan yana basu enci fadin gaskiya ba tare da jin tsoron makircin yan komati ba 


Hassada da bakin ciki itace takesa yan komati su cire malami daga shugabanci  

Duk inda kaga an cire malami daga shugabanci akwai wani  alkhairi daba'a so malamin yaci gaba da samu 


masallacin Apo shine masallaci na biyu Abuja dake unguwar gidajen yan'majalisa tarraya 


Sheikh Nura khalil shine limamin masallacin na farko tun bayan kammala gini masallacin malam musa limamin masallacin National mosque shine ya nada shi limamcin masallacin


Tare dani aka bude masallacin  sheikh Nura khalil yayi kokari sosai wajen raya masallacin da karantarwa ta ilimi mutunne jajirtacce wajen gina al,umma  tun lokacin da aka bawa malam limanci masallacin wasu daga cikin malamai suke masa hassada sunaso suga bayansa  


yanzu don yayi magana kada talaka ya fito yayi zabe matukar ba'a daina kashe  shi ba,meye laifin malam akan wannan magana ba gaskiya ya fada ba ? 


Wannan magana tana tayarwa da duk wani dan' siyasa hankali mai son kujerar mulki,basa son suji ance kada mutane sufito suyi zabe,sai kaji wasu masu wayo daga cikinsu sun fara fakewa da magana addini ko kabilanci idan baku fito Kukayi zabe ba makiyanku  sune zasu samu dama akanku su mulkeku su dinga kashe ku, irin wannan kalmomi dasu suke amfani wajen mulkar jama'a. 


Kullun ina tambaya kaina danamu suka samu mulki mai sukayi wajen kare martabar addini da rayukan jama'a ?


Wanda suka cire malaman daga limanci  babu wata martaba da zasu samu daga wajen gobnati


Malan yana da sabanin fahinta tsakaninsa da wasu malamai  akan wasu fahintoci da yake dasu 

Irinsu:- 

*Taron maulidi  

*Musulmi su daina kafirta juna

*Hadin kai tsakanin addinai musulmi da Kiristoci su hada kai su zauna lafiya su daina kashe junansu 


Irin wannan fahinta da malan yake da ita tasa wasu suna munana masa zato wasu kuma suna kyautata masa zaton alkhairi 


ALLAH ka fahintar damu addini kadauwamar

 damu akan shiriya



Daga malam Kabiru Abdullahi

Sunday 3 April 2022

Hukumar hizba a jihar kano tayi gargaɗi ga musulman da suke cin abinci tsakiyar rana acikin watan ramadan

 Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ci alwashin saka kafar wando ɗaya da matasa Musulmai da su ke ƙin yin azumin watan Ramadan.


A wani sakon murya ta kafar WhatsApp da ya tura wa manema labarai a yau Asabar, Babban Kwamandan Hukumar, Muhammad Harun Ibn-Sina ya ce Hukumar ba za su saurara wa masu karya shari’ar Muslunci da gangan ba.


A cewar sa, duk wanda a ka samu musulmi ya na cin abinci da rana ba tare da wata larura ba to zai gamu da fushin Shari’a.


Ya kuma kara da cewa hukumar ba za ta zuwa ido ta ga a na aikata baɗala a watan Ramadan da ma bayan sa ta ƙyale ba, inda ya ce dole ne ta yi aikinta na horo da kyakkyawan aiki da kuma gani da mummuna.


Ibn-Sina ya kuma taya musulmai a faɗin jihar da ƙasa baki ɗaya murnar zagayowar wata mai alfarma, inda ya yi addu’ar Allah Ya karɓi ibadun Ya kuma kawo zaman lafiya da arziki a ƙasar nan.



Khalifan tijjaniyya sarki sanusi lamiɗo sanusi yaba shugaba buhari muhimmiyar shawar


 Sarki Sanusi Lamido Sanusi

Muhimmiyar Shawara Ga shugaba

Buhari Domin Ceto Kasarmu Nijeriya.

*Ya Kamata Canji Ya Soma Daga

Majalisa


_ Sanata na karbar Naira Miliyan

36,000,000 kowane wata.

Idan aka raba gida biyu yana karbar

Naira Miliyan 18,000,000, ragowar

*Naira Miliyan 18,000,000 za a iya

amfani da su wajen daukar 'yan

Nijeriya 200 aiki kowa ya rika daukar

albashin Naira Dubu 90,000 kowane

wata.*


Idan aka yi mutum 200 sau adadin

Sanatocin mu 109 hakan na nufin za

a dauki 'yan Nijeriya *dubu 21800

aiki *


A takaice 'yan Nijeriya 200 za su iya

rayuwa a wadace da rabin albashin

Sanata na kowane wata.

*Dan Majalisar Wakilai na karbar

albashin Naira Miliyan 25,000,000

kowane wata.*


Idan aka raba albashin gida biyu ya

zama Naira Miliyan 12.5million a

wata. Ragowar *Naira Miliyan 12.5

za ta isa a dauki 'yan Nijeriya 135

aiki su rika daukar albashin Naira

dubu 92,500 a wata*.

'Yan Nijeriya 135 sau adadin yawan

'yan Majalisar Wakilai 360, hakan na

nufin za a dauki 'yan Nijeriya *dubu

48600 aiki*.

Saturday 2 April 2022

An Dauki Nauyin Karatun Budurwar Da Ta Fara Tattaki Daga Bauchi Zuwa Abuja A Kafa, Tare Da Bata Makudan Kudade

 DA DUMI-DUMINTA: An Dauki Nauyin Karatun Budurwar Da Ta Fara Tattaki Daga Bauchi Zuwa Abuja A Kafa, Tare Da Bata Makudan Kudade


Rahoton Daily News Hausa


A yau Jumma'a Amira Ahmad ta hadu da dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a Jam'iyyar APC Farouq Mustapha a gidanshi dake jihar Bauchi.


Idan baku manta ba, a jiya Alhamis "Daily News Hausa" muka kawo muku rahoton Amira Ahmad dake zaune a jihar Bauchi inda ta fara tattaki tun daga jihar Bauchi da niyyar zuwa Abuja domin nuna goyon bayan ta ga dan takarar Gwamnan Jihar a Jam'iyyar APC Farouq Mustapha, tare da karrama 'yarshi kan namijin kokarin da tayi na shiga cikin tawagar talakawa a yayin taron Jam'iyyar da ya gudana a babban birnin Tarayya Abuja.


Dan takarar Gwamnan ya gaggauta dakatar da budurwar inda ya bada umurnin a dawo da ita gida duba da halin rashin tsaro da ake fama dashi, masu dakatar da itan, sun cimma ta a garin Jos suka dawo da ita gida.


A yau Jumma'a Amira ta hadu da dan takarar yayin ziyarar da ya kawo jihar Bauchi inda ya bata mak


udan kudad

Sakon tuni ga yan najeriya daga sanata shehu sanii

 Ikon Allah,Babu irin zagin da ban sha ba,Babu irin cin mutuncin da ban gani ba a lokacin da muka fara magana kan rashin tsaro a Arewacin Na...