Monday 4 April 2022

Cire sheikh nuru Khalid daga limanci ba abinda zai rageshi dashi sedai samun daukaka danasara arayuwa

 Sheikh Nura Khalid


cire shi daga limanci babu abinda zai kara masa sai nasara 


Yanzu na fahinci hikima wasu malamai da suke nemo taimako daga kasa shen waje ko daga wasu mutane abokai ko dalibai su gina musu makaranta da masallaci hakan yana basu enci fadin gaskiya ba tare da jin tsoron makircin yan komati ba 


Hassada da bakin ciki itace takesa yan komati su cire malami daga shugabanci  

Duk inda kaga an cire malami daga shugabanci akwai wani  alkhairi daba'a so malamin yaci gaba da samu 


masallacin Apo shine masallaci na biyu Abuja dake unguwar gidajen yan'majalisa tarraya 


Sheikh Nura khalil shine limamin masallacin na farko tun bayan kammala gini masallacin malam musa limamin masallacin National mosque shine ya nada shi limamcin masallacin


Tare dani aka bude masallacin  sheikh Nura khalil yayi kokari sosai wajen raya masallacin da karantarwa ta ilimi mutunne jajirtacce wajen gina al,umma  tun lokacin da aka bawa malam limanci masallacin wasu daga cikin malamai suke masa hassada sunaso suga bayansa  


yanzu don yayi magana kada talaka ya fito yayi zabe matukar ba'a daina kashe  shi ba,meye laifin malam akan wannan magana ba gaskiya ya fada ba ? 


Wannan magana tana tayarwa da duk wani dan' siyasa hankali mai son kujerar mulki,basa son suji ance kada mutane sufito suyi zabe,sai kaji wasu masu wayo daga cikinsu sun fara fakewa da magana addini ko kabilanci idan baku fito Kukayi zabe ba makiyanku  sune zasu samu dama akanku su mulkeku su dinga kashe ku, irin wannan kalmomi dasu suke amfani wajen mulkar jama'a. 


Kullun ina tambaya kaina danamu suka samu mulki mai sukayi wajen kare martabar addini da rayukan jama'a ?


Wanda suka cire malaman daga limanci  babu wata martaba da zasu samu daga wajen gobnati


Malan yana da sabanin fahinta tsakaninsa da wasu malamai  akan wasu fahintoci da yake dasu 

Irinsu:- 

*Taron maulidi  

*Musulmi su daina kafirta juna

*Hadin kai tsakanin addinai musulmi da Kiristoci su hada kai su zauna lafiya su daina kashe junansu 


Irin wannan fahinta da malan yake da ita tasa wasu suna munana masa zato wasu kuma suna kyautata masa zaton alkhairi 


ALLAH ka fahintar damu addini kadauwamar

 damu akan shiriya



Daga malam Kabiru Abdullahi

No comments:

Post a Comment

Sakon tuni ga yan najeriya daga sanata shehu sanii

 Ikon Allah,Babu irin zagin da ban sha ba,Babu irin cin mutuncin da ban gani ba a lokacin da muka fara magana kan rashin tsaro a Arewacin Na...