Sheikh Nura Khalid
cire shi daga limanci babu abinda zai kara masa sai nasara
Yanzu na fahinci hikima wasu malamai da suke nemo taimako daga kasa shen waje ko daga wasu mutane abokai ko dalibai su gina musu makaranta da masallaci hakan yana basu enci fadin gaskiya ba tare da jin tsoron makircin yan komati ba
Hassada da bakin ciki itace takesa yan komati su cire malami daga shugabanci
Duk inda kaga an cire malami daga shugabanci akwai wani alkhairi daba'a so malamin yaci gaba da samu
masallacin Apo shine masallaci na biyu Abuja dake unguwar gidajen yan'majalisa tarraya
Sheikh Nura khalil shine limamin masallacin na farko tun bayan kammala gini masallacin malam musa limamin masallacin National mosque shine ya nada shi limamcin masallacin
Tare dani aka bude masallacin sheikh Nura khalil yayi kokari sosai wajen raya masallacin da karantarwa ta ilimi mutunne jajirtacce wajen gina al,umma tun lokacin da aka bawa malam limanci masallacin wasu daga cikin malamai suke masa hassada sunaso suga bayansa
yanzu don yayi magana kada talaka ya fito yayi zabe matukar ba'a daina kashe shi ba,meye laifin malam akan wannan magana ba gaskiya ya fada ba ?
Wannan magana tana tayarwa da duk wani dan' siyasa hankali mai son kujerar mulki,basa son suji ance kada mutane sufito suyi zabe,sai kaji wasu masu wayo daga cikinsu sun fara fakewa da magana addini ko kabilanci idan baku fito Kukayi zabe ba makiyanku sune zasu samu dama akanku su mulkeku su dinga kashe ku, irin wannan kalmomi dasu suke amfani wajen mulkar jama'a.
Kullun ina tambaya kaina danamu suka samu mulki mai sukayi wajen kare martabar addini da rayukan jama'a ?
Wanda suka cire malaman daga limanci babu wata martaba da zasu samu daga wajen gobnati
Malan yana da sabanin fahinta tsakaninsa da wasu malamai akan wasu fahintoci da yake dasu
Irinsu:-
*Taron maulidi
*Musulmi su daina kafirta juna
*Hadin kai tsakanin addinai musulmi da Kiristoci su hada kai su zauna lafiya su daina kashe junansu
Irin wannan fahinta da malan yake da ita tasa wasu suna munana masa zato wasu kuma suna kyautata masa zaton alkhairi
ALLAH ka fahintar damu addini kadauwamar
damu akan shiriya
Daga malam Kabiru Abdullahi
No comments:
Post a Comment