Friday 1 April 2022

MAL. NASIR EL-RUFA'I YAFITO YANUNAWA DUNIYA GAZAWAR GWAMNATINSU TA APC AKAN HARKAR TSARO TAREDA NEMAN GAFARAR AL'UMMAR NAJERIYA

 Mun Gaza A Matsayinmu Na Shugabanni Ku Yafe Mana ~ Gwamna El-Rufai Ya Roki Al-ummar Kaduna


Gwamnan Jihar Kaduna a Arewa maso yammacin Najeriya Nasir El-Rufai, ya nemi gafarar al'umma bisa hare-haren da 'yan bindiga da ke ci gaba da salwantar da rayukan a yankunan Jihar Kaduna, musamman harin da aka kai wa jirgin kasa a ranar Alhamis.


Gwamnan, wanda cikin yanayi mai cike da damuwa ya ce haƙiƙanin gaskiya yana cikin matuƙar bakin ciki saboda rabonsa da ya yi bacci tun ranar Alhamis, kuma ba ya iya bacci ko da ya sha maganin bacci saboda tsananin tashin hankali.


El-Rufa'i ya yi waɗannan kalamai ne lokacin da ya je karamar hukumar Giwa domin bai wa al'umma hakuri da ta'azziya da jaje bisa abubuwan da ke faruwa.


Ya kai ziyarar ne ranar Alhamis ƙarƙashin rakiyar mataimakiyarsa Hajiya Hadiza Sabuwa Balarabe da kuma wasu mukarraɓan gwamnatinsa.

Se dai wasu daga cikin matasan kasar najeriya suna ganin wannan ba'abin birgewabane don yafito yanuna gajiyawarsu,kamata yayi su sauka daga kan mukamansu gaba daya,daga cikin masu wannan ra'ayin akwai matashi kwararre akan harkar lafiya kuma mazaunin amerika dakta abdulaziz tijjani.


No comments:

Post a Comment

Sakon tuni ga yan najeriya daga sanata shehu sanii

 Ikon Allah,Babu irin zagin da ban sha ba,Babu irin cin mutuncin da ban gani ba a lokacin da muka fara magana kan rashin tsaro a Arewacin Na...